Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

Daidan Wani: Ba titi ‘yan Kaduna ke bukata ba, a farfado da masana’antu kawai – Inji ‘yan gwan-gwan

Published

on

Shugaban ‘yan gwan-gwan na jihar Kaduna Alhaji Lawal Muhammad Ya’u ya yi kira ga gwamnatin jihar da ta mayar da hankali wajen samar da masana’antu do farfado da wadanda suka durkushe.

Alhaji Lawal Ya’u ya bayyana hakan ne a zantawar sa da tashar Freedom Radio da ke Kaduna.

A cewar sa, farfado da masana’antu tare da gina sababbi zai taimaka wajen samarwa ‘yan jihar aikin yi musamman matasa.

Ya ci gaba da cewa, in har matasa suka samu aikin yi, ba sai gwamnati ta wahalar da kanta ba, wajen gyara tituna, domin al’umma da kansu za su inganta jihar.

Shugaban ‘yan gwan-gwan din yace da yawan titunan da ke fadin jihar al’umma ne suka gina a baya “Chanchangi da kanshi ya gina titunan da ke kewaye da gidan sa ba gwamnati bace ta yi”.

Shugaban ‘yan gwan-gwan din ya ja hankalin matasa da su tashi su nemi sana’ar yi don dogaro da kansu “matasa yanzu su daina tsayawa zaben sana’a duk sana’ar da suka samu su rike ta da zuciya daya”.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!