Connect with us

Labarai

Za mu bibiyi Miliyan 100 din da Gwamnatin Kano ta yi mana alkawari-Gamayyar ‘yan Kasuwa

Published

on

Gamayyar shugabancin kungiyar ‘yan kasuwar jihar Kano ta sha alwashin taimakawa tare da farfado da Kasuwancin ‘yan kasuwar rukunin masu kananan masana’antu na yankin Dakata wadana iftila’in gobara ya shafe su a kwanakin baya.

Jagorancin kungiyar ya bayyana hakan ne a lokacin da ya kai ziyarar gani da Ido na asarar da aka samu wajen tare da bada tallafi don rage radadi ga ‘yan Kasuwar.

Da ya ke jawabi, shugaban gamayyar ‘yan kasuwar ta jihar Kano, Alhaji Sabi’u Bako, ya ce za su bibiya tare da tabbatar da cewar an bada naira Miliyan 100 da Gwamnatin jihar Kano ta yi alkawarin bai wa ‘yan Kasuwar.

A nasa jawabin shugaban kungiyar masu kananan masana’antu ta kasa NAKSI, reshen Kano Alhaji Aminu Ibrahim Kurawa, ya bukaci jagororin kasuwanni da su hada kai  tare da yin duk mai yiwuwa wajen ganin an tallafa wa wadanda suka yi asarar dukiyoyin su sakamakon gobabrar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!