Connect with us

Labarai

Dakaraun Operation Haɗin Kai sun kashe ƴan ta’adda 30 a Borno

Published

on

Rundunar Sojin Najeriya ta ce, Dakaraunta na Operation Haɗin Kai, sun kashe akalla ’yan ta’adda 30 a kusa da Tafkin Chadi a Jihar Borno.

Mai magana da yawun Operation Haɗin Kai, Laftanar Kanar Sani Uba, ya ce sojojin sun kuma lalata wasu kwale-kwale da ’yan ta’addan ke amfani da su wajen zirga-zirga da kai kayan aiki.

Ya bayyana cewa jiragen yakin sojoji sun dade suna sa ido a yankin, inda suka gano sama da kwale-kwale 30 na ’yan ta’adda.

A cewarsa, dakarun sun dauki mataki ne bayan samun sahihan bayanan sirri, sannan suka kai hare-hare ta sama bayan tabbatar da wuraren da maharan suke.

Hare-haren sun lalata kwale-kwalen tare da tarwatsa hanyoyin samar da kayan aikin ’yan ta’addan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!