Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Dan takarar jam’iyyar PDP ke kan gaba yayin da aka samu hargitsi a karamar hukumar Nasarawa

Published

on

Dan takarar jam’iyyar PDP Abba Kabiru Yusuf shi ne a kan gaba yayin da ake cigaba da ‘yaryaga takardun sakamakon zaben gwamnan da ake yi a jiya da daddare.

Yayin da gwamnan jihar Kano Abdullahi Umar Ganduje yake biya masa, sai kuma jam’iyyar PRP take mara mata baya.

Baturin zabe na jihar Kano Farfesa B.B Shehu na jami’ar jihar Kebbi na cigaba da tattara sakamakon zaben kafin a kawo harin tada hargitisi.

Haka zalika rahotanni sun bayyana cewar, sakamakon zaben na nuna cewar jam’iyyar PDP inda take da kuri’u fiye da dubu 951 da dari 531 yayin da kuma jam’iyyar APC ke da kuri’u dubu dari 935,451.

Wanda hakan ke nuna cewar, jam’iyyar PDP ce ke kan gaba.

Yayin da offishin zabe dake nan Kano ya dage zaman tattara sakamakon kawo yanzu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!