Connect with us

Labarai

Dangote na shirin gina matatar mai ta Dala biliyan 17 a Kenya

Published

on

Kamfanin manfetur na Dangote ya sanar da cewa yana shirin gina babbar matatar mai ta kimanin dala biliyan 17 a ƙasar Kenya,  aikin da ake sa ran zai ƙarfafa fannin makamashi a Gabashin Afirka tare da rage dogaro da shigo da tataccen mai daga ƙasashen waje.

 

A cewar kamfanin, an kammala zaɓen wurin da za a gina matatar, ana ci gaba da gwajin ƙasa, yayin da aka fara ayyukan zane da taswirar  aikin.

 

Ana sa ran matatar za ta fi samar da man fetur ga Kenya da maƙwabtan ƙasarta.

 

Kamfanin na Dangote ya ce za a  gina matatar a yankin Lamu da ke gabar tekun Kenya, kuma ana sa ran za ta kasance mai kama da babbar matatar Dangote da ke Nijeriya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!