Connect with us

Labarai

Masarautar Kano ta amince da yin murabus din dagacin Rugu-rugu

Published

on

Mai martaba Sarkin Kano Khalifa Muhammadu Sanusi na biyu ya amince da yin murabus din Dagacin garin rugu-rugu da ke karamar hukumar tudun Wada Malam Bello Muhammad mai shekaru tamanin da biyar a duniya sakamakon rashin lafiya da yake fama da ita.

 

‎Dagacin ya shaida wa sarkin cewa shi ne da kansa ya ke son yin murabus ba wanda ya sa shi saboda yanzu tsufa ya kama shi ba zai iya aikin ba.‎

 

‎Mai martaba Sarkin ta bakin babban dan majalisar sarki Matawallen Kano Alhaji Aliyu Ibrahim yace an amince da yin murabus dinsa da sharadin ba zai kawo wanda za’a nada sabon dagacin ba sai wanda mai martaba sarki ya amince da shi.

 

inda ya ce, ya yarda da hakan, kuma masarautar Kano ta bada damar a shirya yi masa murabus.

 

‎A nasa jawabin Malam Sani Bello da ga dagacin mai murabus ya gode wa masarautar Kano a madadin zuri’ar gidansu bisa amincewarta da yin murabus din mahaifin nasu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!