Labarai
Jigawa: Mutane 7 sun rasu 53 sun jikkata sakamakon iftila’in guguwa

Akalla mutane bakwai ne suka rasa rayukansu, yayin da wasu 53 suka jikkata sakamakon wata iska mai ƙarfi da ta haddasa barna a ƙananan hukumomi 13 na Jihar Jigawa.
Sakataren Zartarwa na Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Jihar Jigawa (SEMA), Hannafi Fagam, ya ce iskar ta shafi gidaje 5,403 a cikin al’ummomi 120.
Ya ce mutanen huɗu sun mutu a Dutse, yayin da aka samu mutum ɗaya-ɗaya a Miga, Ringim da Sule-Tankarkar.
Haka kuma, iskar ta lalata makarantu sama da 47, asibitoci uku, ofisoshin ‘yan sanda biyu da gidaje da dama.
Fagam ya ce gwamnatin jihar ta amince da fitar da kuɗaɗe domin kai agajin gaggawa ga waɗanda abin ya shafa, tare da ci gaba da tantance irin barnar da aka yi domin raba kayan tallafi cikin gaggawa.
You must be logged in to post a comment Login