Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Dr Habib Lawal:Sanya hannun yarjejeniyar cire shingen kasuwanci Afrika zai bunkasa tattalin arzikin

Published

on

Wani masanin tattalin arziki a nan jihar Kano, ya ce, sanya hannu kan yarjejeniyar gudanar da kasuwanci ba tare da shinge ba tsakanin kasashen Africa, lamari ne da zai taimaka gaya wajen bunkasa tattalin arziki musamman wajen inganta bangaren wutar lantarki.

Dr. Habib Lawal Yahya wanda kuma malami ne a kwalejin Fasaha na Jihar Kano, ya bayyana hakan ne ta cikin shirin Labaran ‘Muleka Mugano’ na Freedom Rediyo wanda ya mai da hankali kan batun yarjejeniyar da shugabanni afurka suka sanya hannu a kai a baya-bayan nan.

Ya kuma ce, kamata yayi kasashen Afurka su yi la’akari da yadda sauran kasashen Turawa su ka ci gajiyar gudanar da kasuwanci ba tare da shinge ba, wanda ya taka rawa wajen bunkasa tattalin arzikin nahiyar.

Dr. Habib Yahya ya kuma nanata cewa, matukar aka fara gudanar da shirin na kasuwanci ba tare da shinge ba, lamura za su kyautatu a nahiyar Afurka.

A cewar sa, wannan yarjejeniyar  za ta zaburar da sauran kasashen da ke nahiyar wajen bunkasa tattalin arzikin su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!