Connect with us

Labarai

DSS ta kama shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Bello Bodejo bayan EFCC ta sake shi

Published

on

Lauyoyin shugaban ƙungiyar Miyetti Allah Kautal Hore ta ƙasa, Bello Bodejo, sun zargi hukumar DSS da sake kama shi jim kaɗan bayan da hukumar EFCC ta sake shi.

Lauyan Bodejo, Muhammad Sharif, ya ce DSS ba ta sanar da su dalilin sake kama shi ba, yana mai cewa za su kalubalanci matakin a kotu.

An sake sakin Bodejo ne a yau Juma’a, bayan ya shafe kusan watanni huɗu a tsare bisa zargin halasta kuɗin haram.

A watan Yuli ne wata babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da belinsa, bayan EFCC ta gurfanar da shi kan tuhume-tuhume shida, waɗanda ya musanta.

Kotun ta dage ci gaba da shari’ar zuwa ranakun 5 da 6 da kuma 7 ga watan Oktoban shekarar nan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!