Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

ECOWAS da sojojin Mali sun cimma yarjejeniyar sakin Boubacar Keita

Published

on

Jagororin kungiyar cigaban yammacin Afirka ta ECOWAS da mambobin rundunar sojin da suka yi juyin mulki a kasar Mali sun cimma yarjejeniyar sakin hambararren shugaban kasar Ibrahim Boubacar Keïta.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ruwaito shugabannin sojoji sun bayar da shawarar kafa gwamnatin rikon kwarya ta sojoji wacce za ta kwashe shekara uku kafin daukar mataki na gaba.

Sai dai dubban ‘yan kasar ta Mali sun fito kan titunan babban birnin kasar Bamako ranar Juma’ar da ta gabata, inda suka rika nuna goyon bayansu ga juyin mulkin na baya-bayan nan.

Sojojin da suka kwace mulki a Mali sun ce suna tattaunawa da jam’iyyun adawa da sauran kungiyoyi a kokarin kafa gwamnatin da suke yi.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!