Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Tawagar ECOWAS ta isa Guinea don sasanta rikicin juyin mulki

Published

on

Tawagar kungiyar ECOWAS ta kasashen yammacin Afirka ta isa Guinea.

Ziyarar ta su za ta mayar da hankali domin tattaunawa da shugabannin sojojin kasar da suka yi juyin mulkin da ya kawo karshen gwamnatin tsohon shugaba Alpha Conde.

Ana sa ran tawagar ta ECOWAS za ta bukaci a mayar da mulki ga farar hula a kasar ta Guinea da kuma matsa kaimi kan bukatar gaggauta sakin tsohon shugaba Conde, wanda a yanzu ke tsare a hannun sojoji.

An tsare Conde, tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi masa a karkashin jagorancin Laftanar Kanal Mamady Doumbouya ranar Lahadi.

Sannu a hankali dai rayuwa a babban birnin kasar Conakry ta koma daidai a ranar Alhamis, inda aka sake bude kasuwanni, tare da ci gaban harkokin yau da kullum.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!