Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

EFCC na neman matar Godwin Emefiele ruwa a Jallo

Published

on

Hukumar dake yaki da yiwa tattalin arzikin kasa ta’annati ta EFCC ta ce tana neman mai dakin tsohon gwamnan babban bankin Nigeria CBN Godwin Emefiele tare da Karin wasu mutane uku ruwa a jallo.

Ta cikin wata sanarwa da hukumar ta fitar ta ce ta ayyana neman su ruwa a jallon ne bisa zargin su da hada baki da tsohon gwamnan babban bankin wajen karkatar da akalar wasu makudan kudade mallakin gwamnatin tarayya.

Rahotanni dai na bayyana cewa tun bayan Kama Emefiele tare da gurfanar dashi a gaban kotu ne uwargidan nasa ta yi batan dabo.

 

Rahoton: Mukhtar Abdullahi Birnin Kudu

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!