Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

EFCC za ta gurfanar da Emifiele ranar Laraba

Published

on

Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta EFCC,  za ta gurfanar da tsohon gwamnan CBN Mista Godwin Emefiele a gaban Kotu gobe Laraba saboda ba da izinin buga sabbin takardun naira na sama da miliyan 684 akan sama da naira biliyan 18.

Tun da fari dai an tsara gurfanar da Godwin Emefiele  a  ranar 30 ga watan Afrilu da ya gabata amma aka ɗage ranar bayan yarjejeniyar da aka cimma tsakanin kotun da kuma ɓangarorin biyu.

Hukumar EFCC ta yi zargin Emefiele ya yi burus da umarnin kotu da nufin jefa jama’a cikin mawuyacin hali lokacin aiwatar da tsarin sauya takardun naira da gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta yi.

EFCC ta kuma zargi Emefiele da ba da izinin cirar sama da naira biliyan 124 daga asusun bai ɗaya na ajiyar kuɗaɗen shu=iga na gwamnati ba bisa ƙa’ida ba.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!