Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kaduna

El-rufai ya dakatar da ɗaya daga cikin masu naɗa Sarkin Zazzau

Published

on

Gwamnatin jihar Kaduna ta dakatar da Wazirin Zazzau Alhaji Ibrahim Aminu, wanda shi ne jagoran masu naɗa sarki a masarautar.

Dakatarwar ta biyo bayan amsa takardar tuhumar da aka aike ma sa.

Gwamnatin ta aikewa sauran masu naɗin Sarkin guda huɗu takardar tuhuma da ake buƙatar su bayar da amsa.

Wannan na cikin wata sanarwa da ma’aikatar kula da ƙananan hukumomi da masarautu ta jihar ta fitar.

Ta hannun babban sakataren ma’aikatar Musa Adamu a madadin kwamishina Jafaru Sani.

Labarai masu alaka:

Obasanjo ya kai ziyarar ta’aziyyar rasuwar sarkin Zazzau

Za a yi jana’izar Sarkin Zazzau da ƙarfe 5 na yamma

Masu naɗin Sarkin guda huɗu da ake dakon amsar tuhumar sun haɗar da Limamin Gari Alhaji Dalhatu Kasimu, da Limamin Kona Muhammad Sani Aliyu.

Gwamnatin Kadunan tana zargin masu naɗin Sarkin da ƙin mutunta gayyatar da ma’aikatar ƙananan hukumomi da masaurautu ta yi musu a baya.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!