Labarai
Firaministan Sudan ya maye gurbin wasu ministocin kasar
![](https://freedomradionig.com/wp-content/uploads/2020/07/HAMDAN.jpg)
Firaministan Sudan Abdalla Hamdok ya maye gurbin ministocin kudi, da na kasashen waje, da na makamashi da na kiwon lafiya da kuma wasu manyan ministocin uku, a wani bangare na shirin sake aiwatar da sauye-sauye.
Wata sanarwa da gwamnatin kasar ta fitar ta ce sauye-sauyen na zuwa ne sakamakon bullo da wasu matakai da take ganin za su kawo gyara a sha’anin mulkin kasar.
Mahukuntan kasar dai sun ce sauyin ya zo a bazata, sakamakon cewa ‘yan kalilan ne ke tsammanin maye gurbin Ibrahim al-Badawi, wanda a matsayinsa na ministan kudi ya jagoranci kokarin kawo karshen matsin tattalin arzikin kasar wadda ke fama da rikice-rikicen, inda ya yi hulda sosai da masu ba da tallafi daga kasashen waje.
Heba Ahmed Ali, shine wanda zai maye gurbin Al-Badawi wanda wani babban jami’in ma’aikatar kudi ne kamar yadda sanarwar gwamnatin ta ce.
You must be logged in to post a comment Login