Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Firaministan Sudan ya maye gurbin wasu ministocin kasar

Published

on

Firaministan Sudan Abdalla Hamdok ya maye gurbin ministocin kudi, da na kasashen waje, da na makamashi da na kiwon lafiya da kuma wasu manyan ministocin uku, a wani bangare na shirin sake aiwatar da sauye-sauye.

Wata sanarwa da gwamnatin kasar ta fitar ta ce sauye-sauyen na zuwa ne sakamakon bullo da wasu matakai da take ganin za su kawo gyara a sha’anin mulkin kasar.

Mahukuntan kasar dai sun ce sauyin ya zo a bazata, sakamakon cewa ‘yan kalilan ne ke tsammanin maye gurbin Ibrahim al-Badawi, wanda a matsayinsa na ministan kudi ya jagoranci kokarin kawo karshen matsin tattalin arzikin kasar wadda ke fama da rikice-rikicen, inda ya yi hulda sosai da masu ba da tallafi daga kasashen waje.

Heba Ahmed Ali, shine wanda zai maye gurbin Al-Badawi wanda wani babban jami’in ma’aikatar kudi ne kamar yadda sanarwar gwamnatin ta ce.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!