Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Ganduje ya bukaci hadin kan iyayen yara wajen Allurar Rigakafi

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta bukaci iyayen yara da su baiwa jami’an lafiya hadin kai yayin da ake aikin rigakafin zazzabin cizon sauro, wanda ake gudanarwa a kananan hukumomi 44 na jihar Kano.

Gwamnan Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ne ya bayyana hakan yau, lokacin da yake zagayawa cibiyoyin da ake gudanar da aikin a wasu asibitoci a karamar hukumar Kura, don duba yadda rigakafin ke gudana.

Gwamna Ganduje  kara da cewa maganin rigakafin zai taimaka wajen rage hatsarin kamuwa da cutar zazzabin cizon sauro da ake samu a lokacin damuna.

Labarai masu Alaka.

Ana ci gaba da duba marasa lafiya ta wayar hannu a Kano

Gwamnatin Kano za ta yi rigakafi ga yara sama da miliyan 3

A na sa jawabin shugaban hukumar yaki da cutar mai karya garkuwar jiki a nan Kano Dr Sabitu Shanono, ya yi bayani kan magungunan da za a raba a kananan hukumomin da suka hada da na karin jini da na karin kuzari, sai na kariya daga zazzabin cizon sauro.

Wakiliyarmu Zahra’u Nasir ta rawaito cewa gwamna Abdullahi Ganduje ya kuma ziyarci asibitin karamar hukumar Garun Mallam domin duba yadda ake gudanar da aikin.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!