Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Iyaye su umarci ‘ya’yansu sauraron Rediyo don koyon karatu

Published

on

Wani malamin makarantar Sakandare a nan Kano ya ja hankalin iyaye wajen ganin sun sanya ‘ya’yansu suna sauararon shirye-shiryen koyar da karatu da ake gabatarwa a gidajen rediyo, a sakamakon hutun da aka bayar don kaucewa yaduwar cutar Covid-19 a Kano.

Malam Nura Muhammad ne ya bayyana hakan jim kadan bayan kammala shirin Barka da Hantsi na nan Freedom Radiyo wanda ya tattauna kan shirin koyar da daliban ta kafar yada labarai da dan majalisar Wakilai mai wakiltar karamar hukumar Birnin Kano Sha’aban Ibrahim Sharada ya dauki nauyi.

Nura Muhammada ya kuma kara da cewar duba da koma bayan da daliban ka iya samu a bangaren karatun na su sanadiyyar rashin zuwa makarantar ya sa suka zabo wasu daga cikin muhimman darussa guda shida, da suka hadar da lissafi da Ingilishi, don kara zaburar da su.

A na sa bangaren wani makusancin dan majalisar mai suna Alhaji Abubakar Kingibe, cewa ya yi sun samar da tsrin ne don amfanar da al’ummar jihar Kano ta fannin ilimin.

Ya kuma shawarci dabilan da su mayar da hankali wajen sauraron shirin da ake gudanarwa domin bunkasa fahimtarsu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!