Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gobara ta hallaka ma’aikatan NNPC 7 a garin Benin

Published

on

Wata gobara da ta tashi a kamfanin mai na kasa NNPC ta yi sanadiyyar mutuwar ma’aikatan kamfanin guda 7, a tasharsa da ke Benin a Jihar Edo.

Shugaban sashen yada labarai na kamfanin Kennie Obateru ne ya bayyana hakan ta cikin wata sanarwa da ya fitar yau a Abuja, inda ya ce gobarar ta auku ne a ranar talata.

Kennie Obateru ya shaida cewa tuni aka fara binciken musabbabin faruwar gobarar, kuma sun sanar da dukkan bangarorin da suka dace a kai.

Sanarwar ta kara da cewa shugaban kamfanin man na NNPC Mele Kyari ya mika sakon ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!