Labarai
Gwamna Abba Kabir ya yi Alla-wadai da hare-haren da ƴan bindiga su ka kai sassan Kano

Gwamnan Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya yi Alla-wadai da hare-haren ƴan bindiga da aka kai a wasu sassan jihar, inda ya ce, gwamnatinsa za ta ɗauki matakan da suka dace domin ƙara tsaurara tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.
Wannan na kunshe ne ta cikin wata sanarwa da Babban Daraktan yaɗa labaran gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar, inda ya ce gwamnan ya ce hare-haren sun shafi Chiromawa da ke ƙaramar hukumar Garun Mallam, Beli a Rogo, Bebeji da wasu yankuna da ke kewaye da Gwarzo.
Haka kuma Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jajanta wa waɗanda abin ya shafa da iyalansu, yana mai bayyana hare-haren a matsayin abin takaici da ba za a amince da shi ba inda aka umarci hukumomin da abin ya shafa da su ƙara kaimi wajen tattara bayanan sirri, sa ido da kuma gaggauta kai ɗauki a yankunan da abin ya shafa.
You must be logged in to post a comment Login