Connect with us

Labarai

Gwamna Nasir Idris ya kai ziyara Tsamiya bayan hare-haren ƴan bindiga

Published

on

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris Kauran Gwandu, ya ziyarci al’ummar Tsamiya da ke Karamar Hukumar Bagudo domin jajanta musu kan hare-haren ’yan bindiga da aka kai wasu sassan yankin.

Wata sanarwar da Mai Bai wa Gwamnan na Jihar Kebbi Shawara kan Harkokin yaɗa labarai Yahaya Sarki, ya fitar ce ta bayyana wannan kai ziyara.

Sanarwar ta ce gwamnan ya yi Allah wadai da hare-haren, tare da bayyana cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakan magance matsalar tsaro kuma za ta ci gaba da aiki da hukumomin tsaro domin kare al’umma.

Gwamnan ya ce ya zaɓi zuwa yankin da kansa domin jajanta wa al’ummar maimakon tura tawaga.

A yayin ziyarar, Hakimi Muhammadu Wankai ya nemi gwamnatin jihar ta duba yiwuwar gyara hanyar Kaoje zuwa Illo zuwa Lolo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!