Labarai
Ministan tsaro ya gargadi Gwamnoni kan rabon babura

Ministan tsaron kasar nan, Janar Christopher Musa, ya gargadi gwamnoni da ‘yan majalisu kan rabon babura a matsayin tallafi, wanda yace wasu daga cikinsu na iya komawa hannun ‘yan ta’adda.
Janar Musa ya ce baburan na bai wa ‘yan ta’adda damar yin zirga-zirga cikin sauri da tserewa jami’an tsaro, musamman a yankunan da ke da dazuzzuka da hanyoyin karkara.
Ya kuma ce hukumomin tsaro sun gano wasu kasuwanni da tashoshin motoci ba bisa ka’ida ba, wadanda ake amfani da su wajen safarar makamai da alburusai zuwa wuraren da ‘yan ta’adda ke aiki.
Ministan ya yi kira da a ƙara bai wa ƙananan hukumomi damar taka rawa wajen yaƙi da rashin tsaro, tare da gudanar da tarukan tsaro akai-akai da kuma sa ido kan kasuwanni da tashoshin motoci.
You must be logged in to post a comment Login