Connect with us

Kiwon Lafiya

Rashin shan isasshen ruwa na haifar da ciwon Koda-Dr Faruq Sabo

Published

on

Wani likita a nan Kano ya shawarci al’umma da su rika shanruwa a kalla lita uku a rana domin kiyaye kansu daga kamuwa da cutar  tsakuwar ƙoda.

Dr. Faruq Sabo kwararren likitan Koda a asibitin mafitsara na Abubakar Imam Urology ne ya bayyana haka.

Ya ce ana kamuwa da cutar ne sakamakon daskarewar wasu sinadarai dake cikin firsari, inda suke curewa waje daya a cikin koda su hanata aiki yadda ya kamata.

Likitan ya bayyana ƙarancin ruwa a jikin dan’adam a matsayin babban dalilin da ke janyo cutar tsakuwar ƙoda.

A karshe ya shawarci al’umma da su rika shan isasshen ruwa su kuma  gujewa shan lemukan kwalba da abincin gwangwani domin kaucewa kamuwa daga cutar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!