Connect with us

Labarai

Gwamna Zulum ya bada kyautar gidaje ga ma’aikata

Published

on

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya bayar da kyautar gidaje ga ma’aikatan jinya da malaman makaranta 72 a ƙaramar hukumar Mafa da ke jihar Borno a Najeriya.

Cikin waɗanda suka samu kyautar sun haɗa da wata ma’aikaciyar jinya ƴar ƙabilar igbo da ta kwashe fiye da shekara 24 tana aiki a jihar, Marbel Ijeoma Duaka.

Haka kuma gwamnan ya ɗauki ɗanta, Anthony aiki a jami’ar Kashim Ibrahim da ke Maiduguri.

Gwamnan ya miƙa gidan da kayan da ke cikinsa ga ma’aikaciyar, wadda ƴar asalin jihar Anambra ce, a ranar Talata.

Inda ya ƙara da cewa bata taɓa barin garin na Mafa ko da a lokacin da ake fuskantar hare-haren Boko Haram. Inda ya nemi ta ci-gaba da zama a jihar ko da bayan ta yi ritaya.

Nas ɗin ta miƙa godiyarta ga gwamnan kan abubuwan alherin da ya yi mata da kuma ɗanta.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!