Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Zulum zai dauki ma’aikatan lafiya aiki a Borno

Published

on

Gwamnatin Jihar Borno za ta dauke ma’aikatan lafiya aikin yi guda dari shida da saba’in da nufin kara inganta Asibitocin da ke fadin Jihar.

Gwamnan Jihar Babagana Zulum ne ya bayyana hakan a wani taro da masu ruwa da tsaki na bangaren lafiya da ya gudana a birnin Maiduguri, Jihar Borno.

A cewar Zulum, za a dauke sabbin ma’iakatan Jinya su tamanin da hudu sai kuma Likitoci da ungozomomi dari uku da sittin da biyar, da masu hada magunguna da mataimakasu dari biyar da tamanin da hudu.

Zulum yana mai cewa, daukan sabbin ma’aikatan jinya zai kara wa bangaren lafiya Jihar karsashi wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata baya kula da marasa lafiya sosai.

Daga cikin wadanda suka hallarci tattaunawar akwai kwamishinan lafiya na Jihar DR Salihu Kwayabura da shugaban hukumar ungozomomi Umar Shettima da dai sauransu.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!