Labarai
Gwamnan Jihar Neja ya ayyana dokar hana fita tsawon sa’o’i 24 a Minna

Gwamnan Jihar Neja, Umaru Bago ya ayyana dokar hana fita ta tsawon sa’o’i 24 a Minna, babban birnin jihar, bayan rahoton tashin hankali a wasu sassan birnin.
Dokar hana fitan ta fara aiki nan take bayan Sallar Juma’a, kuma za ta ci gaba da aiki har sai an ba da wani sabon umarni.
Gwamnan ya bukaci mazauna birnin da su kasance a cikin gidajensu tare da kauce wa duk wata zirga-zirgar da ba ta zama dole ba a lokacin dokar hana fitan.
Haka kuma, an bukaci hukumomin tsaro da su tabbatar da aiwatar da umarnin tare da kare rayuka da dukiyoyi a fadin birnin.
You must be logged in to post a comment Login