Labarai
Tinubu ya bukaci a yi bincike kan mutuwar mutane 37 a Neja

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya umarci a gudanar da cikakken bincike kan mutuwar mutane 37 da ake zargi da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, wadanda suka mutu yayin da suke tsare a hannun rundunar Tsaron farar hula ta kasa NSCDC a minnan, Jihar Neja.
Mutanen dai an kama su ne a ranakun 15 da 16 ga Satumba, yayin wani samame da jami’an NSCDC suka gudanar a yankin M.I. Wushishi da Lukoto, da ke Minna.
A cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban kasa shawara kan yada labarai, Bayo Onanuga ya fitar ranar Juma’a, Shugaba Tinubu ya ce rayuwar kowane dan Najeriya tana da muhimmanci.
Ya ce bai kamata wani dan kasa ya rasa ransa a hannun gwamnati sakamakon sakaci, cin zarafi, rashin kulawa ko rashin bin ka’ida ba.
Shugaban ya kuma bayar da umarnin cewa idan bincike ya gano wani jami’in gwamnati ya taimaka wajen haddasa mutuwar mutanen ta hanyar aiki, cin zarafi ko sakaci, a kama shi sannan a gurfanar da shi a gaban kotu.
You must be logged in to post a comment Login