Connect with us

Labarai

Gwamnati ba ta karɓi tuban Abduljabbar ba – inji Baba Impossible

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta ce, ba ta karɓi tuban Malam Abduljabbar Kabara ba.

Kwamishinan al’amuran addini na jihar Dr. Tahar Adamu Baba Impossible ne ya bayyana hakan ga Freedom Radio.

Kwamishinan ya ce, tuban da yayi bai cika sharuɗan tuba ba, saboda haka Gwamnati zata yi hukunci kan sakamakon da ya bayyana a gare ta.

A ranar Asabar ne, aka gabatar da Muƙabala tsakanin Malaman Kano da malamin kan kalaman da ya riƙa furtawa.

Sai dai malamin ya sanar da cewa, ya janye kalaman, kwana guda bayan muƙabalar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!