Connect with us

Labarai

Gwamnatin Jihar Filato ta bayar da umarnin sake bude Makarantu

Published

on

Gwamnatin Jihar Filato ta bayar da umarnin sake bude dukkan makarantun firamare da sakandare na gwamnati da masu zaman kansu a faɗin jihar.

Gwamnatin ta rufe makarantun ne na dan lokaci, sakamakon rahotannin samun wadanda ake zargin sun kamu da cutar mashako wato Diphtheria a jihar.

Kwamishinar yada Labarai ta jihar, Joyce Lohya Ramnap, ta ce za a koma makarantu daga ranar Litinin 14 ga Satumba, 2026.

An dai rufe makarantun ne tun ranar 7 ga Satumba, domin bai wa hukumomin lafiya damar tantance halin da ake ciki tare da ƙarfafa matakan kariya daga yaɗuwar cutar.

Gwamnatin ta umarci shugabannin makarantu da su tabbatar da tsaftar muhalli, tare da sa ido kan duk wata alama da za ta iya nuna cewa ɗalibi ko ma’aikaci ya kamu da cutar.

Haka kuma, ta buƙaci iyaye da masu kula da yara da su kula da tsafta, tare da kai duk wanda ake zargin ya kamu da cutar zuwa cibiyar lafiya domin a duba shi.

Gwamnatin ta kuma yi gargadin cewa bai kamata a rika bai wa wanda ake zargin ya kamu da cutar magani ba tare da shawarar ma’aikacin lafiya ba.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!