Labarai
’Yan ta’adda Goma Sha Bakwai sun mika wuya ga Sojoji a Jihar Borno

Rundunar Sojin kasar nan ta ce ’yan ta’adda goma sha bakwai ne suka mika wuya ga dakarunta a jihar Borno.
Rundunar ta ce hakan na daga cikin nasarorin da dakarunta suka samu yayin ci gaba da gudanar da hare-haren da ake yi kan ’yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata laifuka a sassan kasar.
Daraktan yada labarai na ayyukan tsaro na rundunar, Manjo Janar Michael Onoja, ne ya bayyana hakan a cikin bayanin mako-mako kan ayyukan sojoji.
Ya ce tsakanin ranar 4 zuwa 10 ga watan satumba, sojojin sun kuma tarwatsa hanyoyin samar da kayayyaki ga ’yan ta’adda, tare da cafke harsasai 300.
Haka kuma, rundunar ta ce dakarunta sun samu nasarar kubutar da wasu mutane da aka yi garkuwa da su a wasu sassan ƙasar.
Rundunar ta ce za ta ci gaba da kai hare-hare domin dakile ayyukan ’yan ta’adda, masu garkuwa da mutane da sauran masu aikata miyagun laifuka.
You must be logged in to post a comment Login