Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Jihar Gwambe tayi kan matakin Gwamnatin tarayya

Published

on

Gwamnatin jihar Gombe ta bayyana rashin jin dadin ta kan matakin gwamnatin tarayya na dakatar da shirin samar da wuraren kiwo da kuma tsugunar da makiyaya a wasu jihohin kasar nan.

Gwamnan jihar Alhaji Inuwa Yahaya ne bayyana hakan lokacin da yake ganawar da manema labarai, jim kadan bayan wata ganawar sirri da shugaban kasa Muhammadu Buhari a fadar Villa da ke Abuja.

Gwamnan jihar ta Gombe ya lura da cewa jihar sa tana da Hekta sama da dubu dari biyu da suka shirya bawa gwamnatin tarayya a matsayin tasu gudun mowar don ganin an samu nasarar cimma abinda aka sanya a gaba kan shirin.

A cewar sa akwai manoma da makiyaya da suke bukatar tallafi, musamman wadanda rikice-rikice ya dai-dai ta da har yanzu basu gama farfadowa ba, sai dai yana ganin shirin zai taimaka wajen rage musu radadin da suke fama da shi na asarar da suka tafka a baya.

Gwamna Alhaji Inuwa Yahaya na jihar ta Gombe ya bayyana cewa matsawar aka karbi shirin samar da wuraren kiwon ga makiyaya, shakka hakan zai taikama wajen inganta rayuwar su

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!