Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin jihar Jigawa ta fara biyan ‘yan Fansho

Published

on

 

Gwamnatin jihar Jigawa ta fara biyan yan fansho su kimanin 570 sama da naira biliyan daya.

An raba mutanen zuwa rukuni-rukuni saboda kaucewa cunkoson don rage yaduwar corona da ke yiwa duniya barazana a halin yanzu.

Shugaban hukumar fansho ta jihar Jigawa, Alhaji Hashimu Ahmad Fagam ne ya bayyana haka a jiya Talata lokacin da yake bayyana irin ayyukan hukumar fansho a jihar ta Jigawa.

Alhaji Hashimu Ahmad Fagam ya ce tsofaffin ma’aikatan da za su ci gajiyar shirin sun hada da wadanda suka fito daga jihar da kananan hukumomi a matakin farko.

Ya kuma ja hankalin tsofaffin ma’aikatan da suka samu hakkokin su da su yi amfani da su ta hanyar da ta dace.

Shugaban ya kuma ce wadanda  suka rasu da kuma sauran balas na wadanda suka yi ritaya za a biya kudin a matakin da ake ciki.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!