Connect with us

ilimi

Gwamnatin jihar Kano ta alƙawarta baiwa daliban lafiya aiki guda 146

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta alƙawarta bai wa ɗaliban da suka kammala karatu a sashin nazarin kimiyya da harhaɗa magunguna aikin yi.

Gwamnatin ta yiwa ɗaliban jami’ar Bayero da ke karantar sashin harhaɗa magunguna Waɗanda za su kammala a bana alƙawarin.

Babban darakta a hukumar kula da Asibitoci na jihar kano Dakta Nasiru Alhassan Kabo ne ya bayyana hakan yayin taron bikin yaye daliban da suka kammala karatunsu a sashen.

Dakta Nasiru Kabo ya ce “Wannan wani ɓangare ne na ganin an bunƙasa harkokin kiwon lafiya a jihar kano”.

“Gwamnati za ta ci gaba da bai wa dukkanin waɗanda suka dace guraban aiki musamman a fannin lafiya” in ji Dakta Nasiru Kabo.

Jami’ar ta yaye ɗalibai 146 waɗanda suka kammala karatun su a fannin nazarin kimiyyar harhaɗa magunguna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!