Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

ilimi

Gwamnatin jihar Kano ta alƙawarta baiwa daliban lafiya aiki guda 146

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta alƙawarta bai wa ɗaliban da suka kammala karatu a sashin nazarin kimiyya da harhaɗa magunguna aikin yi.

Gwamnatin ta yiwa ɗaliban jami’ar Bayero da ke karantar sashin harhaɗa magunguna Waɗanda za su kammala a bana alƙawarin.

Babban darakta a hukumar kula da Asibitoci na jihar kano Dakta Nasiru Alhassan Kabo ne ya bayyana hakan yayin taron bikin yaye daliban da suka kammala karatunsu a sashen.

Dakta Nasiru Kabo ya ce “Wannan wani ɓangare ne na ganin an bunƙasa harkokin kiwon lafiya a jihar kano”.

“Gwamnati za ta ci gaba da bai wa dukkanin waɗanda suka dace guraban aiki musamman a fannin lafiya” in ji Dakta Nasiru Kabo.

Jami’ar ta yaye ɗalibai 146 waɗanda suka kammala karatun su a fannin nazarin kimiyyar harhaɗa magunguna.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!