Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano ta raba kayan kula da lafiyar mata kyauta

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta jaddada kudirin ta na cigaba da kula da lafiyar mata masu juna biyu da kananan yara ‘yan shekaru 5 zuwa kasa.

Sakataren hukumar kula da asibitoci na jihar Kano Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa ne ya bayyana hakan a yau, yayin rabon magunguna da kayan aikin lafiya na milyoyin Naira ga wasu asibitocin jihar nan.

 

Dakta Aminu Ibrahim Tsanyawa ya ce gwamnatin jihar kano ta jima tana raba kayan ga manya da kananan asibitocin don saukaka wa al’umma a fannin kiwon lafiya.

Wasu daga cikin wadanda suka karbi kayan, da suka hada da Dahiru Haruna, wanda ke kula da magunguna na asibitin sha ka tafi na Dumbulun dake karamar hukumar Tsanyawa, da kuma wata ma’aikaciyar lafiya dake asibitin kwararru na Murtala, Iya Halliru Haruna, sun bayyana yadda suke yiwa marasa lafiya aiki da kayan.

Yayin rabon magunguna da kayayyakin, asibitin kwararru na Murtala ya amfana da magunguna da kayan aiki na sama da Miliyan 5.

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!