Labarai
Gwamnatin Kano ta ƙaddamar da shirin ziyarar ba-zata a asibitoci

Gwamnatin Jihar Kano ta ƙaddamar da shirin ziyarar bazata a asibitoci domin ƙarfafa ayyukan kiwon lafiya da inganta kula da marasa lafiya.
Wannan na cikin sanarwar da jami’ar hulɗa da jama’a ta Hukumar kula da asibitoci ta jihar Hajiya Samira Suleiman ta fitar.
Sanarwar ta bayyana cewa Shugaban Hukumar, Dakta Mansur Mudi Nagoda ya ce an ɗauki matakin ne domin gyara kura-kurai da kuma tabbatar da bin ƙa’idojin aiki yadda ya kamata.
Hukumar ta ce ba za ta lamunci rashin zuwa aiki ba daga bangaren ma’aikata ba, tare da jaddada muhimmancin mika aiki yadda ya kamata tsakanin ma’aikata domin kauce wa tangarda wajen kula da marasa lafiya.
You must be logged in to post a comment Login