Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Da dumi – dumi: Gwamnatin Kano ta janye dokar kulle

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta janye dokar kulle da aka dauki sama da watanni uku ana yi sakamakon Covid-19.

Biyo bayan rahotannin da aka gabatar a fadar gwamnatin Kano na samun nasara akan yaki da Corona a Kano gwamnatin ta sanar da janye dokar.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan bayan ya karbi rahoton halin da ake ciki a Kano a yanayi na Corona.

Gwamnan ya ce zirga-zirga rika kasancewa ne daga karfe goma na dare zuwa hudu na safiya,.

Ya kuma ce ma’aikatan gwamnati da ke 12 za su fara zuwa aiki daga Litinin din nan, kuma za su rika fita aiki da misalign karfe tara na safe zuwa karfe biyun rana.

Abdullahi Ganduje ya ce masu adai-dai-ta sahu ba a lamunce msu su dauki sama da mutum biyu ba, duk wanda aka samu da karya doka za a gurfanar da shi gaban kotun tafi-da-gidanka.

 

 

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!