Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Coronavirus

Ganduje ya magantu kan sassauta dokar kulle a Kano

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta magantu kan sassauta dokar kulle a jihar da gwamnatin tarayya tayi.

A cikin wata sanarwa da Gwamnatin Kano fitar a daren Litinin dinnan ta ce kasuwanni da wuraren ibada zasu rika kasancewa ne ranakun Lahadi da Laraba da Jumu’a daga karfe 6 na safe zuwa 6 na yamma.

Sanarwar mai dauke da sa hannun kwamishinan yada labarai na Kano Malam Muhammad Garba ta kara da cewa Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ya kira taro da shugabannin kasuwanni game da yadda za a kula da ka’idojin kariyar cutar Corona a kasuwannin

Sanarwar ta kuma kara da cewa ya zama lallai a tabbatar ana amfani da takunkumin rufe baki da hanci da kuma yawaita wanke hannaye a wuraren.

Sannan sanarwar ta ce duk da cewar makarantu zasu cigaba da kasancewa a rufe akwai bukatar dalibai su rika amfani da damar darussan da gwamnatin ta dau nauyi a kafafen yada labaran talabijin da rediyo.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!