Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano ta kara sassauta dokar kulle

Published

on

Gwamnatin Kano ta kara ranar Litinin a cikin ranakun sararawa a fadin jihar.

Gwamnan Kano Abdullahi Umar Ganduje ne ya tabbatar da hakan a wata sanarwa da ya fitar da yammacin ranar Lahadi, ta bakin mai magana da yawun gwamnati Abba Anwar.

Yanzu haka dai ranakun sararawa hudu ake da su a Kano, da suka hadar da Litinin, Laraba, Juma’a da kuma Lahadi.

A cikin sanarwar, gwamnatin Kano ta ce za a rika zirga-zirga daga karfe shida na safiya zuwa shida na yamma a cikin ranaku hudun da aka ware.

Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya ja hankalin al’ummar jihar da su cigaba da bawa gwamnati goyon baya, a yakin da take yi na dakile cutar Covid-19.

Sannan gwamnatin ta kuma gargadi mutane da su cigaba da amfani da takunkumin rufe hanci da baki, bayar da tazara, wanke hannu a ko yaushe da sinadarin wanke hannu.

Umar Ganduje ya kuma bukaci da a cigaba da bin dokokin gwamnati a kasuwanni da sauran wuraren taron jama’a, yayin da gwamnati ke cigaba da lalubo hanyoyin dakile yaduwar cutar Covid-19 a fadin jihar.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!