Connect with us

Labarai

Gwamnatin Kano ta kaddamar da shirin yashe magudanan ruwa domin kaucewa ambaliya

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta kaddamar da shirin yashe magudanan ruwa a fadin jihar gabanin saukar daminar bana ta 2026.

 

Kwamishinan ma’aikatar Muhalli, Al’barkatun Ruwa da Sauyin Yanayi na jihar Kano Dr. Dahiru Muhammad Hashim ne ya jagoranci kaddamar da shirin a yankin Jakara da ke Karamar Hukumar birni a jihar Kano a ranar Al’hamis 04-6-2026.

Kwamishinan ya ce an bijiro da shirin yashe magudanan ruwan ne domin kaucewa ambaliyar ruwa a cikin unguwannin da ke kewaye da manyan kwatoci.

Haka zalika ya kara da cewa, gwamnati zata cigaba da gudanar da wannan aiki a fadin jihar Kano baki yada.

 

A karshen ya nemi hadin kan al’umma domin bayar da cikakken hadin kai a yayin gudanar da aikin.

 

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!