Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano ta kama wani waje da ake ɓoye kayan tallafi kuma ake sauya musu buhu zuwa na siyarwa

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta tabbatar da gano wani waje da ake zargin ana sauya buhunhunan kayan tallafin rage raɗaɗin da Gwamnatin ke rabawa ga al’umma A ƙalla Ƙananan buhunhuna sama da dubu guda aka samu inda ake zargin ana sauya musu buhu zuwa na sayar wa maimakon na kyauta

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ne ya tabbatar da hakan yayin ziyarar gani da ido da ya kai wajen da yake a unguwar sharaɗa.

Da yake jawabi ga manema labarai Kwamishinan Noma Dan Juma Muhamud ya tabbatar da yadda gwamnatin ta tabbatar da kama kayan.

Sai dai Kwamishinan yace har yanzu ba’a san iya adadin buhuhunan da aka kama ba sai dai kawo yanzu ananan ana gudanar da bincike domin tabbatar da adadin su.

Sai dai yanzu an kama samu tsaron wajen da ake zargi tare da su aka haɗa baki domin ajiye kayan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!