Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labarai

Gwamnatin Kano zata kawo karshen barazanar yajin aikin ma’aikata

Published

on

Gwamnatin jihar Kano ta kafa wani kwamiti na musamman wanda zai sasanta tsakaninta da gamayyar kungiyoyin kwadago na jihar wadanda suka bata wa’adin makwanni biyu kan ko dai ta mai dowawa da ma’aikatan jihar kudaden albashinsu da ta rage ko kuma ta tsunduma yajin aiki.

Shugaban gamayyar kungiyar kwadago ta kasa reshen jihar Kano, Kwamared Kabiru Ado Minjibir ne ya bayyana haka, ta cikin shirin ‘Muleka Mugano’ na nan tashar freedom Rediyo da ya gudana a daren jiya.

Ya ce, kwamitin yana karkashin jagorancin sakataren Gwamnatin jihar Kano ne, Alhaji Usman Alhaji.

NLC da wasu kungiyoyi sun shawarci gwamnati kan kudaden Paris Club

NLC:sunyi barazanar tsunduma yajin aikin gama gari

Kwamared Kabiru Ado Munjibir ya kuma ce, tun a ranar juma’a da ta gabata ne suka fara tattaunawa da ‘yan kwamitin domin samar da mafita game da batun rage albashin ma’aikatan a watan da ya gabata.

A ranar larabar da ta gabata ne bayan wani taron gaggawa da gamayyar kungiyoyin kwadagon suka gabatar, suka bayyana rashin jin dadinsu kan matakin da gwamnati ta dauka na ragewa ma’aikata albashi.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!