Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Labaran Kano

Ma’aikata sun yi barazanar shiga yajin aiki a Kano

Published

on

Kungiyar kwadago a jihar Kano ta yi barazanar shiga yajin aikin gargadi na mako guda, matsawar aka gaza cimma matsaya tsakaninta da gwamnatin jihar.

An shirya zaman tattaunawa tsakanin kwamitin gwamnatin Kano da kungiyar kwadago ta jihar domin tattaunawa kan matsalolin da suka dabaibaye ma’aikata.

Shugaban kungiyar kwadago reshen jihar Kano, kwamared Kabiru Ado Munjibir a zantawarsa da Freedom Rediyo ya ce suna sa ran cimma matsaya da gwamnati a zaman su na ranar Litinin.

a cewarsa matsawar aka gaza cimma hakan, shakka babu zasu shiga yajin aiki na gargadi.

Kwamred Ado Minjibir ya ce kungiyar kwadago ta jihar Kano, bata da masaniya game da lokacin da aka fara ragewa ma’aikata albashinsu, ko da yake daga bisani gwamnatin ta nemi afuwarsu.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!