Labarai
Gwamnatin Kano zata kawo karshen rikicin masarauta da ke addabar jihar

Gwamnatin Jihar Kano ta bayyana cewa zata kawo karshen rikicin masarauta da yakici yaki cinyewa a jihar kusan shekaru biyu
Bayanin hakan ya fitone ta bakin kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida Kwamared Ibrahim Abdullahi Wayya inda ya ce gwamnatin zata dauki matakai masu karfi domin tabbatar da zaman lafiya da daidaito game da rikicin sarakunan biyu harma ya ce ana gab da warwarewa
Kwamishinan ya ƙara da cewa akwai yiwuwar wasu daga cikin masu ruwa da tsaki su janye da kansu, ko kuma a cimma matsayar sulhu bisa fahimtar juna.
Ya jaddada cewa gwamnati za ta ci gaba da tattaunawa da dukkan ɓangarori, tare da mutunta doka, martabar masarautu, da muradun al’ummar Kano.
Dangane da sauya sheƙar gwamnan zuwa APC, Waiya ya ce hakan zai buɗe ƙofofi masu yawa ga jihar, musamman wajen samun tallafin tarayya a fannoni kamar ababen more rayuwa, lafiya, ilimi da jin ƙai.
A halin yanzu, Sarkin Kano Muhammadu Sanusi na Biyu na zaune a fadar Gidan Rumfa, yayin da Aminu Ado Bayero ke zaune a fadar Nassarawa
You must be logged in to post a comment Login