Connect with us

Labarai

Gwamnatin Katsina ta sanya dokoki a kan Fetur da POS da cajin waya a Matazu da Musawa

Published

on

Gwamnatin Jihar Katsina ta haramta saye, sayarwa, jigila da ajiye man fetur a jarkoki a fadin jihar tare da rufe sana’ar POS da wuraren cajin waya a Kananan Hukumomin Matazu da Musawa.

 

Hakan na cikin sanarwar da Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan Jihar Katsina, Ibrahim Kaula Mohammed, ya fitar a Daren jiya Litinin.

 

Sanarwar ta ce Gwamna Dikko Umaru Radda ne ya amince da sabbin matakan bayan wani taron gaggawa kan tsaro da ya hada hukumomin tsaro, sarakuna da sauran masu ruwa da tsaki.

 

Ya kara da cewar an dauki matakan ne domin dakile ƴan bindiga da masu garkuwa da mutane, bayan binciken tsaro ya nuna cewa masu aikata laifuka na amfani da man fetur, POS da wuraren cajin waya wajen gudanar da ta’ asar su

 

Gwamnatin jihar ta kuma haramta amfani da babura a Kananan Hukumomin Matazu da Musawa domin rage zirga-zirgar masu aikata laifuka a yankunan.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!