Connect with us

Labarai

Kaduna: Ƴan Sanda sun kama mutane 12 da ake zargi da satar mutane

Published

on

Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna ta kama mutane 12 da ake zargi da garkuwa da mutane tare da kwato bindigogi kirar AK-47 da miyagun kwayoyi a jihar.

 

Hakan na cikin bayanin da Kakakin Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Kaduna, Mansur Hassan, ya fitar a yau Talata.

Ya ce rundunar ta samu nasarar kama mutane 12 da ake zargi da hannu a ayyukan garkuwa da mutane.

 

Mansur Hassan ya ce jami’an rundunar sun kuma kwato bindigogi kirar AK-47 da kwayoyin Tramadol guda 2,700.

 

Ya kara da cewa an kwato motoci guda hudu a yayin aikin da jami’an tsaron suka gudanar.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!