Labarai
Gwamnatin Tarayya da ta Kano za su fara Noman ciyawa mafi daraja

Gwamnatin Tarayya da hadin guiwar Jihar Kano zasu fara Noman ciyawar da Zata fi shinkafa da alkama daraja.
Ministan Bunkasa harkokin Kiwo na Idi Maiha Mukhtar, ne ya bayana hakan a ziyarar aiki a Kano lokacin da ya ke Jawabi ga al’ummar Bagauda da ke Karamar Hukumar Bebeji.
Idi Maiha, ya ce yanzu zamani ne da za a mayar da Hankali wajen bunƙasa kiwo ta hanyar samar da abincin dabbobi bisa haɗin kai tsakanin gwamnatin jahohi da Tarayya.
Ministan tare da rakiyar Kwmishinan Bunkasa Kiwo na Jihar Kano Dakta Aliyu Isah Aliyu,da sauran masu ruwa da tsaki a fanin kiwo.
You must be logged in to post a comment Login