Connect with us

Labarai

Gwamnatin Tinubu na fuskantar caccaka bayan fitar rahoton sabon rahoton IMF

Published

on

Gwamnatin Najeriya na fuskantar sabon suka bayan cece-kuce da ya biyo bayan rahoton Asusun Lamuni na Duniya (IMF) cewa an kashe sama da naira tiriliyan 8 na kudaden gwamnati ba tare da bayyana su a bayanan kasafin kuɗi ba.

Rahotonni sun bayyana cewa, cece-kucen ya fara ne bayan rahotannin da suka danganta ga wakilin IMF a Najeriya, Christian Ebeke, wanda aka ce ya bayyana a wani taro da aka gudanar a Legas cewa an kashe kuɗaɗen gwamnati da suka kai kusan kashi biyu cikin ɗari na Jimillar Arzikin Ƙasa (GDP), amma ba a nuna su a bayanan kuɗaɗen gwamnati ba.

Bisa hasashen GDP na Najeriya na shekarar 2025 da ya kai kusan naira tiriliyan 441.5, adadin ya kai kusan naira tiriliyan 8.83.

Sai dai Gwamnatin Tarayya ta musanta zargin, yayin da ’yan adawa suka bayyana batun a matsayin abin damuwa matuƙa.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!