Labarai
Gwamnatin Katsina ta dauki sabbin Malamai guda 2,158

Gwamnatin jihar Katsina ta dauki sabbin Malamai dubu biyu da dari da hamsin da Takwas da zasu koyar a makarantun Furamare a fadin jihar.
Da ya ke jawabi lokacin da yake miki takardar shaidar daukan aikin ga Malaman, gwamnan jihar ta Katsina Malama Dikko Umar Radda ya ce, sun dauki malaman ne domin kara inganta ilimi a fadin jihar.
Ya kuma ce tun daga shekarar 2023 zuwa yanzu gwamnatin jihar ta dauki ma’aikata dubu bakwai da dari uku da ashirin da uku.
Haka kuma, ya ce, gwamnatin jihar ta tura Malamai dubu ashirin da biyar tarukan karawa juna sani da samun horo na musamman, inda kuma aka tura malamai dubu Talatin zuwa kauyuka.
You must be logged in to post a comment Login