Connect with us

Labarai

Gwamnatin tarayya ta dage zaman majalisar zartaswa na gaggawa da za ta yi

Published

on

An dage zaman majalisar zartaswa na gaggawa da shugaban kasa ya kira don nuna alhini ga rasuwar tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari da aka shirya gudanarwa a yau Talata.

 

Shugaban kasa Bola Tinubu ya kira taron gaggawar ne a jiya wanda za a gudanar a yau, jim kadan bayan sanar da mutuwar tsohon shugaban kasar tare da mayar da shi zuwa ranar Juma’a.

 

Dage taron yazo daidai da lokacin da za gudanar da jana’izar marigayin a mahaifarsa dake Daura shima a yau Talata.

 

Mai magana da yawun shugaban kasa kan kafafen yada labarai Bayo Onanugan ya ce za a kawo gawar shugaban a yammacin wannan rana.

Click to comment

You must be logged in to post a comment Login

Leave a ReplyCancel reply

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!