Freedom Radio Nigeria

Freedom Radio Nigeria

Kiwon Lafiya

Gwamnatin tarayya zata yi duba na tsanaki kan kungiyoyi masu zaman kansu

Published

on

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa zata yi duba na tsanaki kan kungiyoyi masu zaman kan su a kasar nan don tattara bayanan su, sanin adadain su don dakatar da wadanda basa gudanar da ayyukan su kamar yadda ya kamata.

A yan watannin da suka gabata ne dai kudurin dokar yin gyara kan yadda kungiyoyin ke gudanar da ayyukan su, ya gaza tsallakewa a majalisun kasar nan.

Gwamnatin tarayya ta kuma bayyana cewa hakan ya biyo bayan kokarin gwamnatin na tsaftace yadda kungiyoyin ke gudanar da ayyukan su, da kuma dokar da ta hana halarta kudaden haramin da kuma ta’addanci a kasar nan.

Babban Daraktan bangaren binciken masu ta’ammali da Kudaden haramin Francis Usani shine ya bayyana hakan a yayin wani taron kara wa juna sani kan yaki da halasta kudaden haramin da kungiyar da ke yaki da halasta kudaden haramin ta Nahiyar Afrika watau GIABA ta shirya jiya a Abuja.

Mr. Usani wanda kuma shine wakilin kungiyar a Nan Najeriya ya bayyana cewa yin gyara kan kungiyoyin zai taimaka musu tare da kara karfafa ayyukan su.

Listen Live

Freedom Radio Kano 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/t8bhnmek8mzuv Freedom Radio Kaduna 92.9 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/5z9v4k7e9mzuv Freedom Radio Dutse 99.5 FM Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/wp75as7e9mzuv Dala FM Kano 88.5 Your browser does not support the audio element. https://stream.zeno.fm/9zdvuszaanzuv
error: Content is protected !!